Wasanni

Najeria da Kamaru za su fafata a zagaye na 2 na gasar AFCON

Informações:

Sinopsis

Najeriya karkashin  mai horar da kungiyar Jose Peseiro za ta nemi kare maratabar ta da kuma neman ganin ta tsallaka mataki na gaba a wanan gangami,yayida a daya wajen ,Kamaru  a cewar mai horar da ita ,Rigobert Song za su kasance a kan bakar su na ganin su doke Najeriya. A tarihi,haduwar wadanan kungiyoyi Najeriya da Kamaru a shekaru baya suka kasance gagara badau a fagen tamola, Najeriya da Kamru sun hadu sau 22.,Najeriya ta samu nasara a wasanni 11 da ta buga da Kamaru. Yayin da Kamaru ta samu galaba a kan Najeriya sau  hudu Kungiyoyin biyu sun yi canjaras sau bakwai. A tarihin lashe kofin gasar Afirka na kwallon kafa baya ga Masar,da ta lashe Kofin sau 7,Kamaru ta daga wannan kofi sau 5 sai Ghana sau 4.   A bangaren Najeriya,kungiyar Super Eagles ta lashe kofin sau uku, shekarar 1980,1994 sai 2013..Khamis Saley a cikin wannan shiri na Duniyar wasanni,ya mayar da hankali a gasar.